Alqawarin da ciwo


•••Alqawarin da ciwo 1•••


Asalin iyaye na mutanen katagum ne ta jahar bauchi. Gidanmu babban gidane a garin katagum,kuma ALLAH ya albarkaci daukakain zuri'armu da arziki dai dai misali,sakamakon muhimmaci da iyayenmu suka dora akan harkan noma. idan ka shiga gidanmu, zaka iske sassa guda ukku, na farko na wan mahaifina ne baba sada da matansa biyu da 'ya'yansa,sai mahaifiyarsu babanmu itama anan sassan take. Kana matsawa sassan kanin malam sada ne wanda maihaifina ke bi masa . Sai namu sasssan shine na karshe a gidan da mahaifinmu malam habibu da mahaifitarmu inna amina, ita kadaice gun mahaifinmu da 'ya'yansu biyar duk hudun maza ne sai ni kadaice tilon mace a tsakiyarsu. Ni sunana RAHMA amma yawancin "yan gidanmu sukan kirani da Ramatu amma sam babban yayanmu ya hana a kirani da sunana sai dai RAHMA don kuwa yace shine asalin sunana ko a cikin ALKUR'ani. Ranar da aka haifeni mahaifina ya shigo gidan ckn murna don kuwa lkncn da aka haihu yana gona sai wani daga ckn yayyena ya hau keke ya garzaya ya shaida masa. Bakin mahaifina bai iya rufuwa ba sai da yazo ya ganni. Ya dauke ni ya kura min ido tare da tofa min addu'o'i yana mai gdy ga ALLAh DA YA AZUrta shi da samuna sannan gashi na dauko kamannun mahaifiyata, ita asalinta bafaulatanar Ningi ce. Ana cikin murna ne sai ga babban yayanmu mai suna Aliyu ya shigo dakin cikin hanzarinsa bakinsa washe sbd murna,kasancewar duk gayyar 'ya'yan gidanmu babu diya mace sai yau akaina aka fara haifo mace. Mahaifina ya mikowa yaya Aliyu ni ina nade cikin zani , ya amshe ni ckn murna da bata misaltuwa, ya kura min ido na tsawan lokaci yana jinijina irin baiwar kyau da Allah ya bani. Har kusan awa guda ina rike hannun yaya ALIYU(Babansa shine babban wansu mahaifinmu baba sada kenan)

•••Alqawarin da ciwo 2•••



Irin dumbin addu'oin da yaya aliyu ya tofa min a wannna lkn basu misaltuwa, mahaifina ya sake shigowa ya iskeni rungume bisa ikin yaya aliyu, ya dube shi yana murmushi yace'A'A alyu har yanzu kana nan gurun jinjira ne? lallai wannna diya ta iri tuta ta ko dai itace matar?" yayi dryr jin dadi ckn jin kunya aliyu yace "ni wlh baba kyan yrnyr nan har tsoro yake bani, da ace idan ta girma zata yadda da hadin aurenmu ai da sai ince utace natar kawai, don wlh ina sonta babal baba na yayi murmushin gamsuwa da maganar yaya aliyuya dube shi yace" ai shike nan aliyu in dai har kana son diyar nan wlh na dau alkawarin baka aurenta sai dai in kaine da kankakace ka fasa auren amma babu fashi in sha ALLLAHU" Aliyu yayi murmushi ya sake duba na yace'haba baba duk fa ckn zuri'armu ba a taba haifan wanda ya kama kafarta a kyau ba'baba yayi dry yace ' haka dai kake ganmi amma ai kuma kunyo gadon kyau kuna maza n shiyasa kake ganin haka to wanna shine asalin alkawarina ure na da yaya aliyu tun ranar da aka haifeniina ckn tsumma kenan. gsk na tashi cikin kulawa da shagwaba ta ko wane fanni gun uwa da uba kai da dukkan illahirin zuri'ar gidanmu babu ma kamar gun yaya Aliyu. Wai shi dole tattali na yake a matsayin matar da zai aura idan mun girma. Shi yaya Aliyu duk cikin dangin mu shine ya sami isashen ilimin zamani mai zurfi shima a dalilin wani makwabcinmu da ALLAHJ ya hada jinin dansa da yaya aliyu har zumunci mai karfi ya kullu tsakanin iyayenmu. Makwabcin namu Alhaji yakubu mutum ne mai arziki sai ya zama ya koma da shi garin bauchi sbd a lokacin sun kammala karatunsu na sakandire. Duk gidanmu dama su kanyi karatun firamare da na sakandire daga nan sai su kama kasuwanci. Nima ba a bar ni a baya ba na sami yin karatun firamare tare da kulawar Aliyu nake samun daukakar karatuna, don kuwa ya dauki son duniya ya dora a kaina duk zuwan da zaiyi daga bauchi in da yake karatu sai ya siyo min abin da yasan inaso ko kuma wanda zai sani farin ciki. haka kuma baya komawa sai ya tabbatar ya koya min wani abuna daga karatun islamiyyah da boko.


•••Alqawarin da ciwo 3•••


Tun ina yar shekara goma na iya karatu da rubutun hausa haka nan na turanci na kan iya karantwa ko in rubuta. Ina dada girma kyauna yana kara fitowa sutura sai wadda na zaba nake sanyawa kuma iri iri masu tsada shiyasa na fita daban da sauran kawayena,ko kudin scholarship yaya aliyu ya samu duk a kan hidima ta suke karewa. Ina yar shekara goma sha daya yaya aliyu ya kammala karatunsa na jami'a digiri guda biyu ya samu. Ba tare da wani bata lkc ba ya sami aiki a lagos kuma mukami mai girma ya samu. nan da nan ALLAH ya daukaki yaya aliyu ga mota sabuwar yayi ya saya sannan ya gyarawa iyayenmu gidan da muke zaune komai dai yaji a gidanmu. a wannan lokacin da daukakar yaya aliyu tayi kamari shekaru na sha biyu amma zaka dauka na kai sha biyar sbd girman jiki. shi kam maihaifina har ya fara shakku akan al'amarin aurenmu da aliyu sbd yadda yaga yanayin da aliyun ya shga na azurcewani kuma gani ba wani girma nayi ba duk da yake a cewar baba ba zan wuce shekaru sha biyar ba za'ayi aurenmu da yaya aliyu, akwai wani zuwa da aliyu yayi daga lagos lokacin ina zaune a sassan mahaifan aliyu a dakin kakarmu ina ninke mata kayan sawanta kawai sai ganin mu2um nayi yayi sallama ya shigo ckn dakn. sanye yake cikin lallausan bakin boyel sai kyalli yake yi, habawa ban san lkcn da nayi wurgi da kayan dake hannuna ba nayi tsalle na rungume shi tare da fadin "lah! yaya aliyu oyoyo". shima cak ya daga ni sama ya rungume sannan ya sauke ni kasa muna kyalkyala dry ya dubeni fuskarsa cike da fara'a yace,"rahama naji kin kara nauyi ne me su inna suke baki ne idan bana nan?" nayi dry nace,"Allah yaya aliyu duk kayan dadin da kake kawo min ne daga lagos suke sani yin kiba", yayi murmushi yace,"zo mu zauna ki gani ga wasu na siyo miki" muka zauna bisa gadon gwaggo(kakarmu kenan), ya dubeni yace"ina gwaggo ne? nace, "tana bayi yanzu ta shiga" yace" ok, ai na aza ta tafi anguwa ne' ya fiddo min da kwalayen biskit zuwa su chakulet da wasu irin gwangwanaye na biskit wasu na sansu ya saba siyomin irinsu wasu kuwa ma ban taba ganinsu ba, ya bude biskit din kwali yace," bude bakinki kiji irin wannan akwai dadi", ba bude bakin ya bani na gutsura ina ci tare da gyada kai alamun yana da dadi 
ko?" na gyada kai nace, "wlh very sweet". yayi dry tare da ja mini labba yace,"uhm rahaman kwadayi", muka saka dry. nima na dauko biskit guda daya nace," nima yaya aliyu bude bakin ka in baka",ya kuwa bude bakin na bashi muka yi ta dry. ya sauko cakulet yana saka min a baki kenan gwaggo tayi slm ta shigo. hannunsa na bisa baki na muka tsayamuna kallon gwaggo, ta duni aliyu tace," yauwa ka dawo har ka fara sangarta ta ko? sai ka tafi ka barmu da jijalin shagwaba, ka riga ka shagwaba ta da bata abinci a baki shi yasa idan ka tafi take zama da yunwa" ya fiddo ido cikn mamaki yace "ashe zama da yunwa kike yi rahama? to daga yau na daina baki abinci a baki" gwaggo tace"ah! to ku dai kuka sani yrnya 2un tana karama ka koya mata dabi'un turawa ai in agama an kusa ayi aurenku mu huta ku tafi can ku karata". ya ware ido cike da mamaki yace " wana irin aure gwaggo? shekarun rahama fa sha biyu ko kin manta ne? haba ai ko za'ayi aurenmu sai ta kai shekaru sha bakwai zuwa sha takwas". gwaggo tace" ba dai a gidan nan bane za mu bar rahama ta kai shekaru sha akwai tsanani sha biyar, to ba ga sa'anninta ba nan duk an yi musu baiko wasu ma har an sa musu rana" yayi ajiyar zcy a ransa yana tunanin ALLah dai ya taimake shi su bar rahama ta dad girma kafin ayi auren su. tabbasa yasan rahama yake so har kn ransa to amma aurensu ba yanzu ba duk da yake ko sun yi aure ba zama zata yi ba cogaban karatunta na sakandire zata yi har zuwa jami'a maganar haihuwa ma in sunyi aure in sha ALLAHu BABU ITA SAI AN KAMMALA KARATU. GWAGGO TA KATSE MASA TUNANI da cewa, "ali ko dai ka canza ra'ayin aurenka akan rahama ne? naga daga yin maganar auren ka canza fuska kwata kwata" yayi ajiyar zuciya yace " wlh ban canza ra'ayina game da aurenta ba, ai ko don in faranta maku rai zan yarda in auri rahama balle ma har ckn raina ita nake so" gwaggo ta saki wani murmushin jin dadi dangane da maganar yaya aliyu tace, " to Allah ya nufe mu da ganin lokacin auren" yace "amin ba wai na dauke shi da muhimmanci bane, illa dai kawai na kanji dangi nace min matar aliyu nima haka na dauka wani lokacin har baba aliyu na kance masa amma sai inji yace kar in kara kiransa baba sai dai yaya.bayan sun gaisa da gwaggo suka dan taba hira ya kawo irin turarrurrukan da ya kan siyo mata a lagos masu kamshi da tsada ya bata sannan ya riko hannuna muka baro dakinta tana ta shi masa albarka.



•••Alqawarin da ciwo 4•••


Dakin mahifiyarsa muka wuce kuma har a wannan lokacin aliyu rike yake da hannuna muna shiga ta kalle mu tayi murmushi,tace " har kun gama gaisawa da gwaggo" yace" eh, mun gaisa kin san nace maki yanzu bauchi zanje ina son gobe in dawo nan jibi sai in koma lagos" nayi karaf nace" wlh yaya nima zan bika bauchin" ya dubeni yace " kinga yamma tayi bari idan zan sake zuwa sai inje da ke" na make kafada nace " wlh yau na ke so" ganin na bata fuska na soma masa kuka sai yace" come on, meye abin kuka? shikenan je ki shirya kizo mu tafi" innarsu tace " ai dama kai ke bata rahaama gidan nan dole in tace sai tayi abu babu yadda za'ayi ta hanu, yanzu in aka yi auren haka zaka ci gaba da sangartata sai abinda take so za'ayi?yayi murmushi yace, " to ya zanyi inna? kin dai san rahama yarinyace dole in dinga bin lamuranta a hankali kinga yanzu idan ina matsa mata sai ta tsane ni ko an tashi yin auren tace bata so na kinga anyi ba ayi ba kenan" inna ta tabe baki tace " yayi maku dai dai sai kuje kuyi ta kwamacalarku mudai muna nan yan kallone da bada shawara" yayi dariya yana kallona nima shi nake kallo yace "kije ki shirya mana ko ince na fasa zuwa dake" nayi tsalle cikin murna na fice da gudu zuwa dakin gwaggo don kuwaa nan komai nawa yake ku san ma itace ke rike da ni. ina cikin shiryawa ne ya biyo ni dakin gwaggo a lokacin na saka riga ina kokarin zage zip din" ya jawo ni gabansa inda yake zaune a gafen gado har yafara zagemin zip din sai ya fasa yace" gsky ki canza wasu kayan wadannan basu da guga, ina riga da wandon da na siyo maki a lagos"nace " suna nan ban ma taba sawa ba kunya nake ji a ganni da wando kamar namiji" yayi dariya yace "lallai rahama da sauranki to ki shirya idan muka yi aure riga da wando sune kayan sawanki ko anguwa zamu kuwa" na fiddo ido nace" haba yaya aliyu ai sai ayi min dariya duk in da muka shiga" yayi murmushin sa da ke birgeni yace"ai mu a lagos ba ruwan kowa da kowa, kowa harkar gabansa yake yi kinga sai muci karenmu ba babbaka ko? na rike baki abinka ga yarinta sai nace " yaya kare ake ci a lagos din? ya tintsire da dariya har hular kansa na faduwa ya dube ni yace " kai rahama ba dai yarinta da shirme ba. tunda baki gane nufi na ba shike nan a bar maganar maza jeki chanza kayan mu tafi yamma tana yi" da yake dakin gwoggo ciki daya ne kuma kaya na a dakin suke shi yasa dana dauki wanda zansa sai nayi hanyar fita zuwa wani dakin don in canza , sai aliyu ya rikoni ya na dariya yace " lallai rahama wato yanzu an soma girma ba za'a iya tubewa a gaba na ba ko?  yayi kyau da kika fahimci haka" cikin dariya nace" malamin islamiyyan mune fa yayi mana wa'azi yace babu kyau mu nuna tsiraicin mu ga kowa" yace " sai ga wa akace ku nuna? na sha mur nace " ni ban sani ba' yayi murmushi yace " to ai ya kamata ki tambayi malam din don kar insha wuyar fahimtar dake nan gaba" ya sake ni na fice ni ba komai yasa a lokacin na tsane tubewa a gaban mutane ba illa yan nonuwan da suka soma fitomin. amma shekara daya da ta wuce sam bana jin kunyagaban kowa tubewa nake hatta wanka a tsakar gida na kan yi abina tun innata na min fada har ta gaji, yaya aliyu ko da bulala yake ritsani har ya samu na daina.



 Zaune nake gaban motar yaya aliyu akan hanyar mu ta zuwa garin bauchi sai shara gudu yake yi ni kuma sai zuba masa surutu nake yi yana kwasar dariya, ana sallar magariba muka iso gidan Alhaji yakubu inda suka rike yaya aliyu har sai da yasami aiki a lagos snnan ya bar gidan . Duk da yake ina karama suka bar garinmu katagum amma basu manta ni ba haka nima ban manta wasu daga ckn yaran gidan ba. haka suka shiga dawainiya da mu har sai da suka ga mun yi salla mun ci abincin dare sannan hankalinsu ya kwanta. ina zaune cikin yaran gidan a babban falonsu ne yaya alyu ya shigo shi da babban amininsa dan alhj yakubu kuma shine babban da a gidan. kabir ya dube ni yace"sannu rahama bakin bauchi" nayi dry ta na risina na gaida kabir yaya aliyu yace " gata nan yau ta makale mini dole sai ta biyo ni bauchi" suka yi dariya kabir yace "ah! to ai gara ta zama cingam din aliyu tun da ta san kaine mijin" aliyu ya dube shi yace " ki taso muje can gidan kabir sai ki kwana gurin madam din sa" ba'a son ranta ba na mike suma yaran gidan suka rikeni wai su sam kar in tafi sbd sabon da muka farayi da su dama gani bani da bakunta. yaya aliyu ya shiga lallashinsu da cewa " kuyi hakuri gobe da sassafe zan kawo maku ita sai ky yini tare kafin mu koma katagum da yamma " haka suka hakura suka kyale ni muka nufi gidan kabir, duk zaman da suke yi na hira a babban falon gidan kabir da matarsa sakina da yaya aliyu uffan ban iya cewa sbd hirar tasu ta manyace ni nama fi maida hankali na ga kallon da aka saka a falon. kabir da sakina watan su biyu kenan da aure shi yasa sam basu iya boye sirrin soyayyarsu gaban kowa duk yawancin hirar da suke yi na lura sakina sai wani mannewa take a jikin mijinta shi kuma yana yi yana shafar sumar kanta. tsananin haushinsu ya kama ni a raina nace " yau ga yan iska dama abinda suke yi kenan? kai ALLAH ya dai kyauta musu daga sun zama miji da mata kuma sai su kama halin yan iska ni kam ko anyi auren mu da yaya aliyu ba ruwa na da wannan iskanci". na cigaba da sake saken abinyi kawai sai na tsinci kaina da yingyan gyadin karya don dai in bar falon karin cigaba da kallon abin haushi. kabir ne ya fara lura da gyangyadin da nake yi gashi duk na wani takure cikin kujera tamkar mai jin sanyi. kasancewar kujerar 1 seater ce. ya ce "subhanallahi, aliyu mun bar diyar mutane na gyangyadi" ya dubi matarsa yace "sakina a ba karamar amaryanmu gurin kwana" ta mike cikin hanzari tace " duk na san gajiyar hanya ce ta so muje rahama" ni kam duk na kosa in bar falon don tsoro da haushi. cikin tsakar dare na tashi na nemi sakina a gadon na rasa kuma na san tare muk shiga bargo muka yi bacci to ko ina taje oho? sai da safe bayan nayi wanka ina shafa mai sannan ta shigo dakin sanye cikin rigar bacci ta dube ni tace"A'a rahama har kinyi wanka? na ce 'eh yanzu nayi tun cikin dare nake nemanki, ina kike ja? tayi murmushi tare da gyara maballin gaban rigarta ta ce"wlh daga zuwa kaiwa kabir kayan shayi shine bacci ya kwashe ni a dakin sai yanzu natashi" na yi shiru a raina ina cewa, " kya ji da shi kuna can kuna iskancin banzanku, ni na tsane ku yanzu zan bar maku gidanku" ta dube ni tace " bari inje inyi wanka nima' nace" to sai kin dawo" ba tare da na kalle ta ba. mun kasance a babban falon su. bisa dinning table muna yin kalaci cima iri-iri sakina ta shirya mana. muna kammalawa na mike na dubi aliyu nace " yaya aliyu ni dai mu tafi can gidansu ummasalma" (ummasalma kanwar kabir ce kusan sa'annin muke da ita) ya dubeni yace" amma kya bari nima in yi wanka ko? wai meke faruwa ne duk kin wani canza ko shagwabarce zata taso? na sha kunu abina yayi dry tare da mikewa ya nufi kewaye. hakika jama'ar bauchi sun karramamu,musamman iyalan alhj yakubu don kuwa da zamu tafi abin arziki iri iri suka bamu. sbd kaunar da suka nuna min sai naji kamar kar in tafi har kuka sai da mukayi ni da kannin kabir. jininmu ne kawai ya hadu da yaran gidan cikin kwana daya da yini daya da nayi tare da su. bamu isa katagum ba sai bayan sallar magriba kasancewar sai yamma mu ka barbauchi. washegari shikuma yaya aliyu ya koma gun aikinsa a lagos **** ***** ***** ***** 

•••Alqawarin da Ciwo 5•••


Aliyu ke zaune a babban falon gidansa dake birnin lagos, wanka yafito a wannan lokacin da agogo ya nuna karfe biyar na yamma. sanye cikin jallabiya farasal sai dan karamin stool da ke gabansa wanda ke dauke da tiren kayan marmari, ya dauki wani koren apple ya gutsura tare da cigaba da kallon tauraron dan adam din da ya kunna, kararrawar falonsa da yaji ana dannawa shi yasa ya rage sautin talabijn din ya mike yaje ya bude kofar. babban aminisa ya iske a kofar wato sagir gurin aikinsu daya a nan hannu suka tafa tare da dry, suka karaso cikin falon, sagir na cewa " ban yi expecting zan same ka ba na dauka yauma tafiyar dare zaka yo" ya ce " kai last two weeks da nayi tafiyar dare ban ji dadi ba shi yasa nayo asubanci ko 20 mins ban yi da isowa ba" sagir yace" you are welcum" ya ce" 10q" suka zauna aliyu ya turawa sagir tiren kayan marmarin nan gabansa sannan ya nufi firij ya kawo masa maltina da ruwan sanyi. sagir "ai tun kafin in fara da komai bari in isar maka da sakon mutuniyar taka tun da ka tafi ta hana ni sukuni" ya ce" hala taiba don na san ba mai nemana garin nan sai ita" yace " kai ma aikasani cewa tayi mun inzo inyi checking ko ka dawo in yi mata waya yanzu zata zo sannu da zuwa" aliyu ya kurbi ruwa ya aje tambulan din yace" don ALLAH sagir share ta kawai gobe ma hadu ofis don wlh yanzu a gajiye nake ban son tazo tadame ni da surutu" sagir yace" ni kuma gashi zuwa nayi ka rakani gurin mutuniyar kasan har mutanen zariya sun zo ran friday bayan tafiyarka sun kawo sadaki da komai da komai har sun tsaida ranar biki 1 mnth aka sa shine nake so muje da kai ayi arrangin abubuwan" aliyu yace "ashe kayi (serious) akan auren nan? to Allah ya sanya alheri" ya ce"amin" ba su bata lkc ba suka nufi gidansu safiya. asalinta haifaffiyar kano ce aiki ya kawo iyayenta lagos yawancin rayuwarta duk a nan lagos din ta yi ta. washe gari a ofis duk wata hanya da aliyu zai bi ya kaucewa gainin taiba yayi hatta ofis din da ya gargadi masinjansa kada ya bar kowa ya shiga. ba komai yasa aliyu ya tsani haduwarsu da taiba ba illa azalzala masa da take yi da maganar ya aureta shi kuma ya san abu ne mara yiwuwa na farko alkawarin aurensu da rahama abu na biyu kuma sam iyayensa ba zasu amince masa ya auri bayarabiya ba dk da yake itama musulmace to amma da kamar wuya wai gurguwa da auren nesa. yana dawowa gida wanka da sallar la"asar kawai yayi sai ga taiba a gidansa. ya bude mata kofar falonsa tana shigowa ta rungume shi tace ' haba (darling u came back since yesterday) amma sai zilliya kake min a ofis yau, to gani ba biyo ka ko sannu da zuwan nawa ne baka so? ya dan yi gajeren murmushi da bai kai zuci ba sannnan yasa hannu ya banbare taiba daga jikinsa yace" no! ba haka nake nufi ba kinsan yau monday akwai ayyuka masu yawa a ofis dina dole in ga sun kammalu shi yasa tunda kinzo shikenan ko?" ta isa kan kujera 2 seater ta zauna a maimakon ya zauna a kusa da ita kamar yadda ya saba zama a'a sai ya nemi kujerar gefenta ya zauna sannan suka gaisa. Ta tashi da kanta ta nufi firij dinsa dake falo ta bude ta zabo mango juice ta dawo ta zauna tana shan juice tana masa hira amma shi sam hankalin shi baya tare da ita illa ma wasu takardu da yafi maida hankalinsa a kansu yana sa hannu.Ta dube shi tace,"Aliyu yaya su inna a bauchi duk suna lfy? ya amsa mata,suna nan kalau suna gaisheki shi kanshi sai da ya dan murmushi saboda karyar daya shirgawa Taiba yanzu na cewa su inna na gaisheta. Shi koda wasa bai taba furta musu yana neman wata Taiba ba balle susan da zamanta. Murna ce ta bayyana a fuskar Taiba saboda taji surikanta suna gaisheta. Tace, ina amsawa,wai darlin yaushe zaka kaini in gaidasu ne? Gaskiya ya kamata in sansu suma su sanni. Yayi ajiyar zuciya yace, zuwan ki ba zai yiwu ba yanzu ba tunda ba wata kwakkwarar maganar aure tsakaninmu, amma ki bari nan gaba zasu sanki idan kin zama surikar su. Dadi ya lullube ta saboda jin maganar aure yau a bakin Aliyu. Haka dai ta cigaba da damunsa da surutai akan maganar aurensu sai da aka kira sallar magriba sannan tayi niyyar tafiya saboda ganin yayi wo alwala zai fita salla masallaci sannan suka fita tare.





 Duk bayan sati biyu Aliyu ya kan ziyarci mahaifarsa katagum ko yayi kamar ba zai je ba idan ya tuna Rahamarsa da irin shirmenta na yarinta sai kawai yaji ita yakeson gani. Ko yabi jirgi in yamma tayi in kuma ba yamma sai ya tafi a motarsa. Yauma kaman kullum ranar jumaa da hantsi yayi sallama da ofis ya nufi katagum. Karfe takwas na dare ya iso gida dakin Gwoggo ya fara isa saboda duk ya leka dakunan su innarsa bai gansu ba ya iske gwoggo tana jan casbaha ta idar da sallar isha kenan. Yayi sallama ta juyo ta dubeshi tare da amsa sallamar tana cewa, "Ah,ah mutanen ikko barka da sauka. Yace yauwa Gwoggo kuna lfy? Tace Lafiya kalau, zauna mana yace, Ba zama zanyi ba inason in shiga masallaci inyi salla ne, na leka dakinsu inna duk ba sunan lafiya ko? Gwoggo ta sauke mayafin dake kanta zuwa kafada tace, Wlh Ali gidan ba lafiya ina jin duk suna sasan Habibu, kasan Amina ba lfy to wlh jikin yaki dadi. Ya fiddo ido yace,"subhanallah, meke damunta? Anje asibiti kuwa? Duk haka ya jerowa gwoggo wadannan tanbayoyin guda biyu tace, To gashinan dai ciki ne gareta tana shan wahalarsa shine jiya jini kuma ya tsinke yana ta zuba muna kyautata zaton bari ne to rashin ganin gudan cikin ya fito shi yake samu kokwanto dama gobe ake shirin zuwa asibitin idan jinin bai tsaya ba, Duk Aliyu yabi ya firgice ya dubi gwoggo yace, bari inyo sallah sai mu tafi asibiti yanzu, yaushe ne zaa zauna da mutum a gida yana zubda jini, ya fice cikin sauri ya nufi masallaci. Kafin ya dawo gwoggo ta shiga sasanmu take sanar da mu zuwan Aliyu. Jin haka yasa naji dadi a raina nasan mai lallashi na yazo don kuwa tunda inna ta fara ciwo na sukurkuce sai aikin kuka saboda nayi mugun shakuwa da inna ta.Yana shigowa dakin innata na isa jikinsa da sauri na kwakume shi ina kuka ya rungume ni yana lallashi, shima yaya Aliyu idonsa ya kada yayi ja saboda irin yanayin ciwon da ya gani na innata. ko zama bai yiba yace su fito da ita a tafi asibiti a lokacin duk iyayan mu maza suna nan sukace ya bari sai gobe tunda dare yayi sannan shi kuma gashi tattare da gajiyar tafiya yace shi sam bai amince ba dole suka hakura da tashi shawarar aka nufi babban asibitin Bauchi da ita a wannan daren. Naso in bisu don har Yaya Aliyu ya saka ni a motar amma babana yace sam bai dace aje dani ba, haka na hakura na shige gida da gudu ina aikin kuka ganin haka yasa Aliyu ya biyo ni ya lallasheni sannan yaja motar suka tafi, washe gari ranar asabar itace ranar da bazan taba mantawa da ita ba a tarihin rayuwata. Ranar bakin ciki, ranar kuka, ita ce ranar da na gwammace in koma ga mahaliccina. Ina zaune a dakin innarmu bayan na gama share dakin na goge leda ko ina na tsaftace shi sai na yi wanka na shirya tsaf abina ina jiran dawowar su yaya aliyu daga bauchi don in sake binsu zuwa ganin innata a asibiti domin tun da suka tafi jiya basu dawo ba illa baba sada ne kawai ya dawo da safe ya shaida mana an kwantar da ita. Ashe bayan tahowarsa bai fi da awa daya ba ALLAh ya amshi ran mahaifiyata. Ni dai ina zaune a dakin sai naji hayaniya a tsakar gidan mu ina shirin fita inga ko menene sai na ci karo da yaya aliyu ya kutso kai ckn dakin idonsa yayi jawur tabbas kuka yayi inna ta lullube cikin zani aka shige da ita uwar daki. duk da yake bani da wasu shekaru masu yawa amma hakan bai hana ni fuskantar inda aka sa gaba ba. Tabbas inna rasuwa ta yi haka naji zcyta tana gaya min. na dubi aliyu a firgice na ce "ya aliyu mene ne sam yaki yarda mu hada ido illa kawai ce min yayi" sun sallameta ne? nace " ta mutu ko? tambaya ta ta tsorata yaya aliyu sai yace ' waya gaya miki? karya ne' mahaifi na najiyo daga ckn daki suna maganar likkafani habawa sai na kankame aliyu ina gunjin kuka nace ' haba yaya aliyu gashi nan ance ta mutu kana cewa karya ne, wayyo ALLah na yau na shiga uku! ban kuma sanin in da kaina yake ba sai da yamma lis bayan an kai inna kushewar ta. ganin nayi kwance bisa cinyar yaya aliyu yana tofa min addu"o"i yana ganin na bude ido yayi ajiyar zcy yace,"sannu ko rahama,yanzu me ke damunki? na bude baki na da kyar nace " yaya aliyu ina inna ta ke? ya dan yi jim tamkar ba zai yi mgn ba har sai da na sake maimaita tambayata sannan yace " tana daki" to kai ni in ganta, taji sauki? abin da nace kenan ido na kyar kansa yayi saurin cewa " an maida ta asibiti' na tashi daga jikinsa na zauna nace " gashi na hango m2ne cike da gida sannan zakace inna bata mutu ba? ni wlh na san ta mutu boye min kake" sai hawaye ke zuba min shar shar ya kwantar dani a kirjinsa yana share min hawaye tare da aikin lallashi na. tabbas sai anan ne na dada sakankancewa inna ta rasu ina tausayin kai na sai dai nafi tausayawa " yan kanni na guda biyu. mutuwa kenan mai raba da da mahaifi ta raba masoyi da masoyi 'kwana biyu da rasuwr inna duk na fita hayyaci na snd mugun sabo da shakuwar da muka yi da inna shiyasa ake cewa ba mutuwa akewa kuka ba sai sabo shi dama turken wawa ne. na kode na jeme sbd rashin cin abinci ina zaune a takure can sakon gadon gwaggo sai ga yaya aliyu ya leko dakin daga ni sai gwoggo ne a dakin ya isa inda nake a takure ya gurfana gabana yana duba na yace" rahama kin ci abinci? na gyada kai alamar eh ya dubi gwaggo yace wai taci abnci gwaggo? ta girgiza kai tana duba na tace ' sam bata ci komai ba ina ga tun kokon safe shima kadan ta sha gashi yanzu ana neman karfe ukun rana' ya kada kai ckn damuwa yace ' in akwai abinci bani yanzu zata ci shi' gwaggo ta miko masa shnkafa da miya ckn langa tace " kila da yake kai ne ta ci amma ni nayi lallashin duniya taki ci har fushi nayi don taci abinci amma a banza" ya amshi abnci tare da ckli ya zauna gaba na ya soma bani abincin da kyar nake ci sai ina jin abincin har wani daci yake min a baki, sai da yaga na koshi sannan ya kyale ni. ya je dakin sa ya kawo min katuwar gora ta (five alive) da babban gwangwani na biskit yace idan na kasa cin abinci sai in dinga ci. yadda kasan ban rasa mahaifiya ba haka na koma a gidanmu, kowa ka gani lele na yake babu ma kamar gwaggo da ta shiga sangarta ni tamkar ni kadaice jikarta. sai abn da naga dama nake yi a gidan nan sam bata son taga an takura ni yanzu ta hau fadan ni marainiyace, shi yasa ma riko na kacokan ya koma hannunta. kakanni na na gurun uwa sun so kwarai su tafi dani can gurinsu a ningi in zauna amma fafur gwaggo ta kiya, hakama kanwar mahaifiya ta da take aure a garin bauchi ta so a bata ni kasancewar itama 'ya'yanta duk maza ne amma sai bata sami nasarar dauka ta ba gwaggo ta hana kowa. A wannan lkcn shekaruna sha uku daidai yadda na taso da kiba yanzu duk sai na rairaiye na zama yar siyat sai kyau da na kara wai nice har samari ke kawo min daukin neman aure gun babana amma ya kan basu hakuri yace ya riga yayi min miji yaya aliyu. Duk wanda yaji ance zan auri yaya aliyu mamaki yake yi sbd haduwa irinta yaya aliyu ga ilimi ga tsafta ga kyau ga kwarjini wasu har abin dry abin yake basu wai babban ma'aikaci kamar aliyu ne zai auri yar ficikar yarinya kamata kai lallai yaudarar iyayen mu kawai yake yi in ma auren alkawari ne to sun cuceni don kuwa nan gaba kara aure zai yi ni ko in wulakanta basu san shine alin bane da kansa ya furta yana sona tun cikin tsumma kuma har yanzu wannan kalmar ta so tsakanina da aliyu bata gushe ba a zuciyarsa nima kuma raina ya na son dan yayan nawa ko don sbd yadda yake tattali da riritani ako da yaushe. 


•••Alqawarin da Ciwo 6••


 Yau juma'a na yo kwalliya ckn leshi da yaya aliyu yayi min da salla, bkn wata kawata hanne ake yi har an kai ta gidan miji yau ne ake mata jere nima sauri nake in tafi duk da na san yaya aliyu na bisa hanya. ina fitowa soron gidanmu muka yi aringizo da shi zai shigo hannun sa rik da yar jakarsa yayyane ke biye da shi da kaya niki niki bauhunna abin masarufi ne rinsu suga,. omo , shinkafa, katan katan na taliya kai tarkace dai irin wadda ya saba kawowa iya yenmu daag lagos, ya dubeni ckn shai'awa yace " a 'a yar matasa ina zuwa? ko kwalliyar juma'an tar abn mai gida ne? to ga ni na iso" muka tintsire da dry ban sami gaya masa inda zani ba sai na amshi yar jakarsa muka dawo ckn gida yana rike da hannuna. ya isa dakin gwaggonmu ya wuce aka shiga jero masa kayan abinci fankasau kawai naga ya cini ka mina zaune a gefa ina kallonsa har ya kare sannan ya dubeni yace " wai ina zaki na naga har da yafa mayafi? na gaya masa inda zani ya rike baki ckn al"ajabi yana duban gwaggo yace " yanzu gwaggo da gske an yiwa hanne kawarta aure? tace " kwarai kuwa shine abin mamaki? yace" haba gwaggo wai me yasa har yanzu kun kasa gane illar da auren wuri ke jawowa, ki duba kiga fa kawarsu jummai da akai mata auren wuri inace gunrin haihuwa ta zama yar yoyon fitsari sbd bata isa haihuwa ba wannan ma kadai ai ya ishi iyaye ishara su dinga barin "ya" ya suna kaiwa shekaru sha takwas shine munzalin aure yanzu don Allah ina ranar jummai anan an cuceta an cuci rayuwarta gashi naji ance babu rai ya zo sbd wahala, haba don Allah"GWoggo ta numfasa ta ce " a gaisheka bature koko ince likita bokon turai.wannnan irin sharhi? to mu wannan shine gata ga ya'yanmu ba gara muyi masu aure ba da suje su dauko mana abin gori" ya ce " ni ina gani duk wannan ya danganta ga irin tarbiyya da iyaye suka ba yaro ne ko kuma sakaci daga garesu,amma babu wani maganar dauko abin gori, kuma yawanci iyayen mu mata ai su sukejanyowa kansu abin gori sbd dorwa 'ya'ya mata talla a madadin zuwa makaranta kinga kuwa dole yara su lalace can gurin yawon tallace-tallace. ni kam ina gdy ga Allah da yasa mu ana gidan baku da wannan dabi'ar ta dorawa yara talla abu daya ke damuna yanzu game da karatun rahama ina son ku kyale ni in nema mata makarantar gaba da firamare ta kwana a garin bauchi tunda ta kammala firamare" gwaggo ta kwabe baki taba jinjina kai tace" sam ban amince ba tun lokacin mahaifiyarta na da rai bamu amince ba balle yanzu da bata da rai, ai sai ka jawo mana abin surutu da zagi a garin nan yaushe ne zamu yadda ka dauki rahama yar shekara sha uku ka kaita wani gari wai karatu shima ai zubda mtunci ne ina marabar dambe da fada, da talla da makarantar kwana? ya ce" wlh da akwai maraba sosai gwaggo kinga makarantar kwana idan kaje tamkar kana gaban iyayenka ne tunda baka ayi sakaci da yaro ba balle har ya fita ya dauko abin kunya  tsabar kara2 da koya tarbiyya shi ake koyawa sabanin 'yan talla da suke shiga tashar mota da kasuwa suna felle rashin kunya son ransu ba kwaba balle tsangawam haka zaki ga yarinya ta zage tana zagin kato sbd ya sayi abinta ya hana ta kudi ko kiga ta kama shi da kokowa duk muna kallonsu a tashoshin mota da kasuwanci to ina ranar wadannan muggan dabi'un? wlh garin kokawe-kokawenna ne zaki ga sha'awa ta ingiza wani katon dama ba mata gare shi ba yaja yar mutane sako ko wani shagon ya lalata ta kinga shi ai talla bai tsinanan komai ba daga karshe idan akayi rashin sa"a yarinya ta riga ta saba da cudanya da maza da kashe kudi shi kenan ta sami hanyar bin maza. Yayi tsaki ckn takaici yadda kasan ni ake dorawa tallar, gwaggo tace' mu dai babu dayan da zamuyi ba talla babu kuma wani zurfin karatu ga diya mace sai aure mu shi muka sani kuma shi muka gada kaka da kakanni muma ta hanyarsa aka same mu kaga ko ai ba maki aure ba" yadda ka san in saka hannu aka in yi ta zunduna ihu haka nakeji sbd jin gwaggo ta kafe ba zanyi karatun boko ba, ni kam buri na ke nan ba ni son aure tun daga kan abin da ya sami kawata jummai na yoyon fitsari duk kuma musabbabin auren wuri ne sai ina rayawa a raina tabbas kila nima haka ce zata same ni tunda gwaggo ta kafe ita ra'ayinta na aure kuma babana ba shi da zabi sai gwaggo.





Abu daya ya kan sani jin dadi a raina idan na tina cewa yaya aliyu na za'a aura min kuma shi mai son ayi karatu ne to kaga kenan bani da matsalar karatu sai ta wajen haihuwa na runtse ido na ckn tafukan hannayena tamkar zanyi kuka, yaya aliyu ya fuskanci nufi na na son yin kuka sai yace " rahama taso muje ki wuce gidn bkn nima zani inyi sallar la'asar. shi a tunanin sa hanani tfy da yayi shine musabbabin bacin raina bai san hirar su da gwaggo ce ta tada man hankali ba. muka fito ya shiga ya gaida su innarsu sannnan muka nufo kafar gida anan ne muka hadu da babana aliyu ya risina har kasa ya gaida shi baba yace ' ikon Allah ashe ka iso grn" yaya mutan ikko da ikin naka yace lfy kalai baba" yace " madallah idan ka kintsa ina son ganin ka" yace " to baba bari in yo sallah" baba ya shige ckn gida ni kuma muka wuto jkn motar yaya aliyu ya fiddo kudi sabbi ' yan naira goma-goma na dubu daya ya mika min yace" gashi sai ayi haidmar biki ko? na sa hanni biyu na amsa nayi gdy, ya nufi masallaci ni kuma na koma gida na ba gwaggo kudin dannan na tafi. mahaifina sun kebe da yaya aliyu a dakin kofar gida bayan sallar isha'a baba ya dubi aliyu yace dama ba wani abu yasa nayi kiranka ba sai game da maganar rahama, shin har yanzu kana son ta? aliyu ya gyada kai yace ' kwarai ina sonta baba ni ban ma taba tunanin zan dai na son rahama ba "yace toh alhmdlh tunda kana son rahama,kuma wai sbd mu iyayenku kake sonta ko ra'ayine na kanaka, shin kayishririn auren rahaam? aliyu yace eh to gsky baba ni banyi shirin komai yanzu ba illa shirin karatu nke mata ina son in samo mata mkrntr yammata ta garin bauchi sai ta cigaab da karatunta tunda nasan ko za a yi mgnr aurenmu sai nan gaba kaga lkcn ko ai uku ta kammala ya isheta idan akayi auren sai ta cigaba da karatun" baba yayai ajiyar zucy uace " wannan shine ana dara ga dare yayi, ai yanzu ba maganar cigaban karatu ga rahama illa zamcen aure shiyasa nayi kiranka don inji naka ra'ayin idan ka amince za'a daura aure ka tafi da matarka in yaso tayi karatun can a dakinka tunda shine burinka" nana da nan zufa ta karyowa yaya aliyu sbd jin wannan kalamai na mahaifina ya share zufar data tsattsafo masa a goshi da hannunsa ya ja numfashi a lokaci guda yace " baba ko ka manta shekarun rahama sha uku ne yanzu yace kwarai ina sane ban manta ba cancantar hakan shi yasa na sanar da kai ban sani ba ko ka canza ra'ayinka kanata"ya ce ni sam ban canza ra"ayi na ba amma a tawa shawarar ina ga zaifi kyua a dan bar ta ta kara dan girma ko nan da shekara biyu ne kaga lokacin ta kai shekara sha biyar baba yace wlh aliyu da ra'ayi na kenan amma sai rasuwar uwar yarinyar nan ya ruguza komai kaga yanzu ikon rahama ya koma hannun gwaggo babu mai tsawatawa rahama a gidan nan yanzu gwaggo ta hau sababi tace za a takurawa marainiya, ba wai na raina rikon da gwaggo take mata bani illa yanzu sai abinda take so take yi a ckn gidan nan ko ni ka mina tsoro kar wata ran a wayi gari rahama ta dauko mana abin kunya sbd sakacin tarbiyya kaga gara in yi mata aure hankali na zaifi kwanciya shi yasa na shaida maka in kana yi ayi da kai don kuwa masoya sun fara sintiri har da mai gari na son ta mahaifinsa ya aiko kuma wlh kowa ya zo na kan shaida masa nayi mata miji kaga da muguwar rawa gwanda kin tashi, kar su ji haushin na hana su aurenta su yaudareta su lalata mana ita ko su hure mata kunne ta bijire mana shi yasa gara ayi auren mu huta" 

•••Alqawarin da Ciwo 7•••


Har yanzu Aliyu zufa yake yi shi sai yana jin mgnr tamkar a mafarki wai yau shine da auren rahama yar shekara sha uku abin da bai taba kawowa a ransa zai faru nan kusa ba.ya shiga jerowa baba illar auren wuri ke kwowa amma sam baba ya kiya sai ma ce masa yayi ' ai ni aliyu gara ko me zai faru da rahaam ya same ta a dkn mjnta sabanin ya sameta a gabanmu, in har son da kake wa rahama na tsakani da Allah ne to gra ka amince da aurenku in kuma ba haka ba to ni daman na san yaudararmu kke yi kamar yadda mutanen gari ke zunden hakan, kaga sai in nemi wanda zai rike min ita tsakani da Allah in bashi aurenta" kwakwalwar aliyu tayi caji tare da daukan zafi snnan zuiyarshi ta sosu don jin wai mutanen gari na zunde akan irin son da yake wa rahama nan take yba baba tabbacin zai aure ni amma sai yace " shi kenan na amince dari bisa dari da aurenmu da rahama amma ina neman alfarma ka a daura gobe kamar yadda nai kace ayi hkr har sai sati na sama idan na dawo sai a daura ranar asabar in yaso lahadi sai in tafi da ita. kuma kar kuyi wahalar yi mata wani abu komai da zata bukata zata same shi a can idan ma babu zan siya mata baba yace haab aliyu ai ko da muke iyayenka gaba daya ai ba a yi haka ba ydda akewa duk wata 'yar gata muma haka zamuyi wa rahama ko don kare mutuncin ta a can gaba" aliyu ya dago manufar baba da yace can gaab wato kar ya goranta min wata rana amma sai yace " haab haba baab yaushe ne gani a raye zan bari kuyi wahala akan auren rahama ai ko ba ni ta aura ba ni ya kamata in yi mata komai na kayan daki balle ta zama mallaki na. ina son ku kwantar da hankalinku da zarar an daura aurenmu rahama kadia zan tafi da ita ba tare da komai na dawainiya ba ina son ma tun yanzu ka sanar da yan uwa" baba dai murnace ta coko masa ciki sbd jin kalaman aliyu sannan babban abin farin ciki yadda ya nuna halacci akan maganar iyaye bai biire masu ba duk da yake shima yana so auren washegari maganar aurenmu da yaya aliyu duk ta watsu ckn danginmu kowa sai yake da wannnan aure babu kamar gwaggo wadda sbd murna guda ta dinga rangwadawa ni ko muna zaune gefenta kawai sai na saka mata kuka ni a dole ba na son aure. don gsky ko da can da ake cewa aliyu zan aura ni a wasa nake daukan abin sai yau ne na tabbatar gsky ne da naga ana ta rabon goro da alawa, sannan naji ana cewa wai da an daura zai tafi dani lagos. wlh ba komai yake sani kuka ba sai idan na tuno da jummai kawata wadda a sanadin aure gashi ta nakasa gurin haihuwa, shikenan nima yanzu da anyi auren idan nazo haihuwa zan sami matsala duk da yake ma ni a lkcn ban san komai game da aure ba. na cigaba da aikn kukana gwaggo ta matso daf da ni tadafa kafadata tana lallashina tace " haba yar lelen gwaggo meye kuma abin kuka daga zancen aure? ko ba kya son yaya aliyun nake ne? na dago ido na yayai jawur nace " ni gwaggo ya zaku ce wai zai tafi dani lagos ni kadai ni wlh ba zan bi shi ba" gwaggo tace " toh shikenan ni zan shirya idan aka daura auren mu tafi tare sai ya hada mu mu biyu kin yarda ko? na yi saurin gyada kai nace " na yarsa kema acan zaki zauna ko? ta ce kwarai kuwa" sai da ta gama lallashi na da dadadan kalamai sannan ta dauki buta ta fita.




 a bakin kofa suka hadu da yaya aliyu zai shigo dakin. Tace " yauwa Ali sai ka shiga kayi lallashi mutuniyar ka kukan aure take? yayi murmushi yace " yanzu gwaggo dan Allah waye ya tabo min amarya kin san fa yarinyace? tace wlh babu wnd ya tabo ta ganin ana raba goro da alawa shine ta saka kuka" ya shigo dkn ya zauna daf dani ya riko hannuwa na ckn nasa yace " haba rahamata ko ba kya so na ne? na dago ido na da suka jajir na kalle shi ga wasu sabbin hawaye na zuba amma bance uffan ba ya sake cewa" kina so na rahama na gyada kai na tabba cin eh yace ok to kiyi hkr ki daina kuka babu abun da zai same ki idan akai maki aure ko wani yace maki wani abu zai samekine? na girgiza kai yace to gaya min abinda ke saki yin kuka ko kina tsoron wani abun ne? nayi saurin cewa eh" ya dan fiddo ido yace " me kike tsoro? nace "ni haihuwa nake tsoro" kawai sai naga ya tintsire da dry yace " wa ya ce maki zaki haihu? nace" ba ina gani kowa aka yi mashi aure haihuwa yake ka duba fa yadda jummai ta zama yanzu tana can abitin kano za a yi mata aikin ni wlh tsoro nakeji" na sake rushewa da kuka ya kwantar da kaina bisa kirjinsa yana share min hawaye yace " come on, ki kwantar da hankalinki, in dai haihuwa kike tsro(i promise yhu ) nayi maki alkwari ba zaki haihu da wuri ba in Allah ya yarda sai a lokacin da kika kai munzalin haihuwa (do u agree)? kin amince? na gyada kai ya ce to yi min yar dryr nantaki mai ban sha a wa" bansan lokcn da na kyalkayle da dry ba d dai dai lkcn gwaggo ta shigo tana kallonmu ta ce " iko sai lillahi rahama yo ina kukan?anya wannan ba zaki kwacen dan saurayin mijin ba?? mu ka sa dry gaba dayanmu. A gaskiya aliyu ya shiga halin rudani da ya koma lagos, don kuwa ckn sati gudan da baba ya diba masa don har " yar rama sai da yay. ba wai baya son aure na bane illa kankanta da yake ganin nayi, daga gida har ofis baya samun walwala ya rasa yadda za'ayi ya sanarwa da abokansa na lagos yadda yake daukan kansa mai bala in aji a birnin lagos yaushe ne zai iya furta musu zai auri yar shekara sha uku. tabbas yawancin frnds dry zasuyi masa sbd yadda matsayinsa yake. ya so ma ace ya gayawa aminisa sagir to yana shakkar kar ya gaya masa shi kuma ya gayawa amaryarsa safiyya kaga daga nan tonon silili yazo kenan. shi kam dole aurenmu ya zam na sirri har sai yaso don kansa sannan zai bayyana ni ga abokansa a lokacin da ya tabbata idan suka ganni sai sun san ya iya zaben mace aliyu ya shirya kansa ckn kaftani a shadda ya isa gidan sagir da misalin karfe takwas na dare. Bisa teburun cin abinci ya iske su suna cin sbinci, safiyya ta sha ubansun kwalliya na wani(lace) tayi kyan amarci har ta gaji sai yaji innama ace yadda rahamansa ke da bala in kyua gaka take babba ga waye wa,gsky da sai tafi safiyya hadewa tunda zai dinga sai mata kaya masu tsadar gske, sai dai kash kafin yaga rahama cikakkiya haka za a kwashi shekaru biyar koma fiya da haka. sagir ya mike ya tarbo shi ckn fara'a suka zauna dinin table din ya dubi safiyya yace " amarya kin sha kamshi yaya amarci? ckm mirmushi tace " amarci gamu nan a cikinsa tsundun" suka yi dry ta mike ta shirya masa abinci a gabansa ya dube ta yace " kayya safiyya gsky da kyar zan iya cin abinci nan bana jin dadin jikina" sagir yace " wai meke damunka ne ckn satin nan duk wani (so weak) nake ganinka? yayi dan gajern murmushi yace " kai dai barni kawai sagir probs na iske barkatai a katagum abn ba dama" ganin bai fito fili ya sanar da sagir matsalar dake katagum ba sai shima ya bar zancen illa kawai yace " to Allah ya kyauta kuma ya jisshe mu alheri amma don Allah kayi kokari ka ci abinci ko yaya yake ni kaina bana jin dadin ganin ka haka duk da ban san problems din ba ( but yhu must try to eat)" ganin sun takura shi sai ya soma cin abincin amma sam baya jin dadin abincin ko rabi bai ci ba yaji bai iya ci gaba da ci dole ya hakura ya dinga kwararawa cknsa tacaccen ya yan itatuwa. hirar ma sama sama suke yi, safiyya ta dubi aliyu tace " shin aliyu ko ka sami min wata yar kawa ne? ni naga tunanin naka(so deep) ne yayi dan yake yana dubanta yace ' ta iya yiwuwa haka ta iya yiwuwa kuma ba haka ba abin ne wani iri( i don't knw hw to explain but tym will tell) tace " au haka ne abin yar boyo? yace kingane ko safiyya wata yarinyace nake nema ckn wasa ashe iyayenta sun yi (serious) da batun shine suka ce in fito ayi mana aure to ni kuma a shekaru na sai ina ganin ban isa aure ba ko safiyya ta tintsire da dariy har da kyakyatawa ta dubi sagir tace " dear kaji wani shirme gun wannan tsohon tuzurun in yarinyar bata ce kayi mata tsufa ba ai ka auna arziki ko ni yanzu ai tsoho na aura don dai ina son abi na haka ne amma yaushe? suka yi dariya sagir yace ' yanzu nan safiyya nine tsoho? to ki sha kuruminki kwanan nan zan karo maki kanwa wadda tafiki yarinta under 16 zan auro sai ki tabbatar cewa yanzu irinmu 'yan mata ke nema ido rufe" ta shagwabe fuska tace " don ALLAH na tuba dear kar muyi haka da kai daga wasa sai tsole ido" sukayi dry duk wata damuwa da aliyu ke tattare da ita ta kau sai jefi-jefi da yakan tuno nan da sati war haka ya zama ango.

•••Alqawarin da Ciwo 8•••



 Yana zaune a ofis din sa ranar alhamis ana gobe zai tafi katagum ke nan yayi bala in zurfi ckn tunani gashi dai gobe zai tafi amma har yau ckn abokansa babu wnd ya san cewa zai yi aure shi bawai auren ne bai so ba ila kankantar rahaman  da yake gani. Nan take sai ya tuno da babban amininsa a bauchi wato kabir yayi hanzarin janyo wayrsa ta (landline ya latsa ko minti guda ba'ayiba ya samo layin kabir suka fara da gaisuwa sannan aliyu yace "KB yaya madam? kai ma ya kake da bauchi?" yace " everything is fyn ai nayo zaton ba zaka neme ni ba in yaso ranar daurina auren sai mu hadu a katagum sai in ga abokin da ya finin" aliyu yace " oh kb am sori wlh ayyuka ne sun yi min yawa a ofis ashe ka sami labarin daurin auren? ya ce nima jiya alhajinmu yake sanar mani su baba na katagum sun aiko masa da gron daura aure shine nima na sani, aliyu (what is happening) ne akan auran nan? ya ja dogon numfashi yace, "kai dai bari kawai kabir wlh kai kanka shaida ne ina son rahama (too much but) ni ban shirya mana aure yanzu ba (last week) na zo ma su baab da maganar zan sama mata (boarding scul) ana bauchi to anan ne nana ya ke sanar da ni shirinsa na aurenmu gsky kuma na amince da hujjar da ya kafa min na dalilin auren amma don Allah kabir ina son kar ka sanar da kowa maganar auren na don kuwa zai zamo (in secret) ckn sirri ka gane ai?" yace gsky(i don't understand wat u mean) shin ko kacanza ra'ayin aurenka da rahamar ne? gsky yarinyar is very nice ga tsabar kyau ni ina ganin nan da 2 yrs idan kayi kiwonta sosai zata yimaiko har ka gaji moriyar ta" suka sheke da dariya abin ka ga shakiyyan abokai aliyu yace" wlh (i never change my mind but the prob is) ka san ni da nuna matsayi akan komai nawa (could u imagine frnds) anan lagos dariya zasu min idan suka san zan auri yar shekara sha uku? (dat is y) na ke son kayi (taking care ) daga kai sai sakina ne ckn frnds dina suka san auren nan. kabr ya sauke wani gwauron munfashi yace" kana ganin haka zai yiwu? shin ina ka taba ganin aure ya boyu ko ayi zaman aure ckin sirri? ina ce lagos zaka kai rahama? kana ganin zai kyautu ka boye ta gidanka ba tare da kowa ya sani ba? ya ce " kwarai zai yiwu kai dai ka taimaka min da abinda nak so daga baya zan sanar da kai (plans) dina" yace" shi kenan sai mun hadu a katagun" aliyu yace "yaushe zaka zo? Ina ganin nima gobe da yamma zamu isa can sbd daura auren na safe ne" yace " amma gida zaka bar sakina ko? yace " kai zai wuya in bar ta a gida ita kanta tana son zuwa katagum din kaga daganan sai su raka amarya lagos ko? aliyu yace"what! dn Allah ka rufa min asiri akan zancen kai amaryan nan kai ana abu cikin sirri zaka janyo tonon silili. gsky ko su baba na shaida masu bana bukatar 'yan rakiya wa rahama daga ni sai ita zamu tafi duk mai son zuwa gidanmu ya iya zuwa daga baya" kabir yace '" gsky ni aliyu na rasa inda kasa gaba, anya kuwa kana son yarinyar nan ko dai auren dole su baab zasu hada ba su sani ba? ni kam ina tausayawa rahama irin zaman da zatayi a gidanka muddin baka son ta illa biyayyar iyaye yasa ka aureta. don ALLAH aliyu in baka son yarinyar nan ka gaya min wlh na san yadda zanyi in fahimtar da su baba su hakura da auren yanzu" yayai murnushi har sautin ya isa kunnen kabir yace "wlh, wlh kaji rantsuwa kanen? ina son rahama tsananin so kuwa ta yadda bana jin zan iya rayuwar aure ba tare da ita ba kuma ina tsammanin ko ckn tsumman goyo aka ban auren rahama zan iya amsa inyi rainonta har ta girma a hannuna bale yanzu na tabbata rainon da zanyi mata bai wuce(2 to 3 yrs) ba kafin mu soma zaman aure na sossai sbd haka kr kayi kokwanto akan auren muko na dole ne don biyayyar iyaye ina son ka saka shi a cikin ire iren auren soyayyar daka sani kamar irin naka da sakina kil ma ya zarta naku" suka yi dry, kabir yace shin wani abu da bangane ba shine maganar rainon da naji kana cewa zakayi wa rahamar(i don't understand)?" ya murmusa yace " kar kayi kokwanton abinda nace . Zanyi rainon raaham har sai naga ta zama mace sosai sannan zan fara dora mata lalurar aure kaga tayi girma ta sami ishasshen ililmi akan abin ka gane yanzu? ya numfasa yace " kwarai na gane manufarka, amma abin da kamar wuya yadda kake gwauro a bakaa auren wadda kake so sannan kace zaka zura mata ido kai ban yarda ba kunma ba zan taba yarda ba" aliyu ya keec da dariya yace " ni kam zan iya kuma wlh wannan alkawaru ne nayi in sha Allahu sai na cika shi(5 yrs) zan diba ma rahamar kaga lokacin zan nemi hakkina (she is 18) ai yayi ko? anan kama kabir yayi dry iya son ransa yace" kwarai yayi daidai amma wlh wannan alkawarun da ka dauka wa kanka nasa masa suna ALKAWARIN DA CIWO! kuma sai ka fadi haka da bakinka. to wai tsyaa idan ita rahama ta nemi hakkinta fa ya zaka yi?" yace " nasan zai yi wuya ta nema sbd na lura bata san komai ba game da sha'anin aure kuma tun yanzu tana min kuka wai ita tsoron haihuwa take yi tunda kawarta ta zo hihuwa ta zama yar yoyon fitsari kaga ke nan na sami madogarar da zan dinga kafa mata hujja ina tsorata ta da abun in kuma har ta matsa shi kenn" yace " wlh aliyu wannan alkawarin da ka dauka zai yi wuya kuma n tabbata kafin rahama ta bata kai ne na farko na san kuma kai ne zaka sha wuyar alkawarin" suka yi dry gaba daya sun kusan fin awa guda suna hira a waya daga karshe sukayi sallama.




Haka aliyu yaci gaba da shirye shiryen zuwa katagum daura auren sa ba tare da ya sanar wa da kowa ckn abokansa ba balle gurin aikinsu. shi ko dan irin hutun nan da angwaye suke dauka na cin amarci bai nema ba sabod yasan shi ba wani amarcin da zaici tunda kwna biyu kacal zai yi a katagum sai ya dauko amaryarsa zuwa gidnasa lagos.sagir ya kusa ya dago abin da ke faruwa da yage setin akwatuna a dakin baccin aliyu amma da yake wayom aliyu ya zarta misali sai ya juye shi bai bai ya shirya masa karyae na wani cousin dinsa ne y siyo masa zai yi aure. taiba kuwa har kuka tayi sbd ganin aliyu ya rame a ckn satin nen. Ana sauran kwana daya daurin aure na da yaya Aliyu ya iso garin katagum,ranar jumaa kenan da misalin karfe bakwai na marece lkcn sallar magrib,ko cikin gida bai shiga ba ya nufi masallaci don yin salla.Tare suka jero da babana daga masallaci zuwa gida suna tafe suma tattaunawa gane da daurin aurenmu gobe.Dakin da yaya Aliyu kan sauka na soro nan suka shiga shi da baba,ya nuna masa akwatunan da ya yomin na aure guda hudu shakare da kaya masu tsadar gaske yawanci duk dinkakkune tun a lagos ya bada aka dinka sannan ya fiddo rafar kudi yan dari bibbiyu na dubu ashirin ya mikawa baba yace,gashi baba wannan sadakin rahama ne,baba yana rike da kudi a hannunsa yace,"haba Aliyu yaushe ne kana dan mu har sai ka bada sadakin rahama.To ka bar abinka kayi wata hidimar ni ba zan amsa ba",Aliyu yace,"Aa baba baayi haka ba sadaki ai shine aure kuma ya zama dole a ba rahama sadakinta muddin ina son aurenta tunda ba sadaka kuka ban aurentaba ba kuma ko sadaka ne dole diya take ba baiwaba ta cancanci sadaki''.Baba yayi ajiyar zuciya yace, kwarai na san da haka ko auren sadaka da ake bayar wa ai dole a biya sadaki balle ma ku kuna son junanku. A matsayi na na kanin mahaifinka ni zan biya sadakin.Yayi saurin cewa aa baba wlh na yafe maka tunda ina da hali na ni dai fatana ku dinga mana addua kuna sa mana albarka tare da fatan ayi a saa.Yace shikenan Allah yayi maka albarka ya albarkaci auren ya ce amin baba. Aliyu ya nemo yan matasan gidanmu suka jida Akwatunan suka shige dasu cikin gida dakin goggo shi kuma na biye da su da dan kit a hannunsa.A lkcn ina takure bisa gadon goggo ina rusa kuka sbd yan uwa da suka tasani gaba wai sai sun samin lalle.Aliyu yana shigowa suka tasa shi gaba da tsiya wata abokiyar wasanmu tace,lah!lah!me zan gani?yanzu nan angonne da kanka dauke da akwatin kayan lefen?lallai zamani ya canza maimakon kayi kiranmu mu zo mu kawo shine ka kawo da kanka?ina ganin ma amaryar bari mu kai makaba kai ne zaka kai abarka chan legos din,Yayi murmushi duk da yake Aliyu sam ba mai son surutu bane valle irin wadannan wasannin abokan wasa inkaga yawan maganar aliyu to a gaba na yake ko kuma ana magana akan abinda yashafeni.Ya dubi msi maganar yace,Au baba bai gaya muku babu yan kai amarya ba?Daga ni sai ita zamu tafi in yaso daga baya zanzo da kaina in kaiku kuga wuri sukace gsky mu wannan tsarin bai mana ba,ya zaka maishe mana ya tamkar ba yar dangi ba gashi ita kenan mace a gidan kamar rai daga rahma fa an gama auren ya mace a gidan nan don Allah yaya aliyu kayi hkr ka barmu mu raka ta muna son ganin birnin ikko,Yayi dan murmushi cikin ire iren murmushinsa masu burgeni in dai bai amince da maganarkaba haka yake irin wannan murmushin yace shikenan zamu tattauna dasu baba za'a san abinyi. Ni kam ina leken sa ta cikin mayafi na ashe ya hankaltu da ni sai naga yayi saurin aje akewatin hannunsa ya nufo inda nake ya zauna a gefen gadon yasa hannunsa yana kokarin yaye rufar da nayiwa fuska ta yace"Amarya ba dai har an fara kukan amarcin ba ne tun yanzu?Yana cire mayafin yaga fuskata sharkaf da hawaye nan da nan sai naga ya hade rai ya juya ya kalli wadanda ke shirin sa mani kalle yace"Yanzu don Allah har kun farasa yarinyarnan kuka tun yanzu?gsky zamu bata da wanda yasata kuka shin me kukayi mata hafsa?Tace wlh babu illa dai sa mata lalle da muka zo yi shine abin kuka mu kuma wlh sai mun sa mata tunda muma haka aka yi mana"Yace a kan al'ada kawai sai ku sa min ita kuka? Ina dai sa lallen nan bawai ya zama dole bane to yau akan rahams an dai na,suka sheke da daria shi kuma ya juya ya ci gaba da lallashina na da cewa yi shiru kinji baby na babu mai bata miki jiki da lallen aure in dai ina gidannan sai dai in sun yarda in sa maki da kaina. 

•••Alqawarin da Ciwo 9•••


Suka yi dariya tare da cewa,ai zaka iya tunda ma lefen da kanka ka kawo.Ke kam rahama kinyi sa'ar miji mai tattali da lallashinki Allah yasa ya dore haka"suka fice suna dariya shi kuma ya cigaba da lallashi har da hirarraki har sai da yaga dariyata sannan ya nufi sassan mahaifinsa.Yana fita danginmu tare da su gwoggo suka antayo cikin dakin don ganin kayan lefe na. Kaya kam sun amsa sunansu kowa sai tofa albrkacin bakinsa yake tareda sam barka masu mamaki nayi sbd irin yawan kayan tare da haduwarsu. ni kaina duk da a lillibe nake sai da na dinga liken kayan ta ksan mayafina. lallai yaya aliyu ya jibgo mini kaya na gani na fada. Ina jin masu kirgwa suka ce zannuwa kala talatinne cif. duk sakankance gurin ganin kaya ashe masu niyyar sa mana lalle basu fasa ba sai ji nayi sun yaye lullubi na sun goga min lalle tare da fesa min nono daga bisani suka feshe ni da turare. In banda aikin kuka babu abin da nake yi. Karfe takwas na dare su kabir da sakina suka iso kasancewar suna da dangi da kuma gida a katagum shi yasa suka sauka a gidnsu. washegari da misalin karfe tara na safe aka daura aure na da yaya aliyu. wlh ni tamkar a mafarki nake ganin abin ban tantance da gaskiyar haka ba sai da naji abokan wasa na rangadamin guda suna cewa yau na tabbata matar aliu gobe sai lagos sannan ne na saka kuka sbd jin zan tafi wata uwa duniya lagos in bar iyayena . ni kam dari bisa dari ina son yaya aliyu illa lagos din ne bana son inji ana cewa zan tafi. ni a son samu nama a ce bayan auren a nan gidanmu zan zauna shi kuma ya dinga zuwa kamar da amma ina babu yadda za'ayi haka ya faru. ban sami ganin yaya aliyu ba sai bayan sallah isha'i aka sani nayi wanka aka bani wata tsaleliyar atamfa ckn kayan aure na na saka sai sheki da kyalli na keyi ni kaina na san na kara kyau a ranar fiye da nawa na baya. aliyu ma da ya shigo dkn gwaggo ya ganni rudewa naga yayi har yana rayawa a ransa anya zai iya cika alkawarin daya kudirta a ransa na kyale ni?


✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨


Gsky da yana ganin nayi kankantar aure amma yau sai ya ga na kara yi masa girma tamkar yar shekara sha biyar ko sha shida da ma ganu da manyan gabobin girma irin na mahaifiyata. ya tsaya kusan minti biyu yana kare min kallo sama da kasa ni kam kaina a sadde yake a kasa gaba daya yau kunyarsa na ke ji. daga ni har shi kamshin turare muke mai dadin gske. haka nan ya daure yace " rahama' na amsa ckn sanyin murya " na'am" gabansa sai da ya ba da ras! da yaji murya ta domin yau itace rana ta farko da murya ta ta sa shi jin sanyin jiki ya sake cewa " raahama yau kuma baki iya kallo na sai dukar da kai ko nayi laifi ne baki ganni ba tun bayan daura aurenmu? na yi saurin dago kai nace masa" ni wlh ba haka bane" yace " to menene? nace " ba komai" yace " ko kunya ce " na gyada kai nace "uhm" yayi dariyarsa ta kasaita yace" yanzu nan kunya ta kuma kike ji rahama? ashe abn da sake wai an baiwa mai kaza kai. to bari kiji yanzu ni aliyu na zama mijinki tsakanin mu babu zancen jin kunya duk wata damuwarki ni zaki gayawa tunda yanzu dani zaki zauna. kinga gobe idan na tafi dake gida na can lagos to komai ya kare najin kunya daga ni sai ke zamu zauna babu su gwaggo ko su baba a kusa kila ma sai kin haihu zaki zo gida su ganki, haba wa kaman jiransa nake sai kawai na saka masa kuka shi kansa da ya san maganar da yayi zata sani yin kuka na tabbata da bai fade ta ba. kuka na shiga yi ba kadan ba duk ya bi ya birkice ya shiga ckn rudani ya ce " subhanallahi! meye abin kuka don nace ba zaki ga su gwaggo ba ko don nace zaki haihu? to yi hkr ni sam na manta kina tsoron haihuwa ba zan yarda ki haihu ba kinji? bil hakki da gskiya ni fa tsoron haihuwa nake har bana kaunar in ji ance wani ya haihu. da yaga na dan tsagaita da kukan sai yace" ba kya son ki bini lagos ki ci gaba da karatun ki? nace " ina son karatun amma ni bana son tafiya lagos dinne idan munje wanene zai taya ni zama? yace " ni zan taya ki ko ba kya so? nace " ina so to idan ka tafi gurin aiki fa ya zanyi? ya ce " ai inajin a lokacin ke kuma kin fara zuwa makaranta, kinga lokacin da zaki dawo nima na taso aiki ba shike nan ba idan na dauko ki a makaranta sai mu wuce gida abin mu" nace " dawa zan dinga kwana?" yayi murmushi yace " dani mana ko ba kya so?" na dan yi murmushi nace " ina so" washegari lahadi da aka wayi gari na ga ana ta min shirye-shiryen tafiya ga dangin mahaifiyata sun ce aladole ko mtum biyu ne sai sun raka ni gidan miji na, shi kuma yaya aliyu ya tubure sam baya son ' yan rakiya. dole haka kowa ya hakura ni dai bani da wani aiki ranar sai kuka sbd jin wai ni kadai zan tafi sai aliyu wanda ko duk kawaye na da ake masu aure dangi da kawaye ke raka su gidan mazajensu har ma a kwana amma ni yaya aiyu ya hana. su gwaggo da iyayenmu maza sune suka tasa mu gaba ni da yaya aliyu suna man nasiha" baban aliyu shi aliyun yafi tsananta fada da nasihar akansa yace"don Allah abba (sunan da su kan kira aliyu da shi kenan sbd sunan kakanmu ke gare shi) ya ci gaab " ka kula da amanar yarinyar nan kar ka kuskura ka ci amanarta ko musguna mata don Allah ka kula da addininta duk da yake na san rahama akwai son addini to amma kayi kokari ka kula sosai. mu dai nauyinta ya tashi a kanmu ya koma gare ka to kar kayi sakaci ka bi ta sannu a hankli sbd ka san yarinyace akwai tsabar kuruciya a tare da ita, Allah ya taya ka riko ya baka zama lfy kuma ya albakarkci auren" gaab daya dakin aka ce amin. baba na shima yayi mana nasiha shima kaninsu yayi mana sannan suka fice daga dkn sai mu sai gwaggo. itama ta dora da tata nasihar daga karshe tace ' to mai gida na ga dau yar kanwarka nan ka bi ta sannu kan hankali na tabbata zaku yi zama lfy tunda ku na son juna. amma don ALlah ka rage irin sangarta rahama da kake yi sbd yanzu zaman aure zaku yi ya ban banta da irin zaman da kukeyi da. ke kuma ban hana ki shagwaba ba amma ban da rainu da rashin kunya, kar ini kar in gani in ba haka ba ni in zo in amshe mijin inyi zama na a lagos ke kuma ki dawo nan dakin" muka yi dan murmushi sai a nan ne na san nayi murmsuhi amma da kuka kawai nake yi. haka aka sako ni gaban motar yaya aliyu ina ta aikin kuka yan uwa suka zagaye motar suna mana Allah kiyaye hanya. kabir ma yace suna na zuwa shida sakina. muka yi sallama da yan uwa motar mu ta daga ni daya tilo kamar yar mayy sai aliyu. motar jeep yar karama mai(tint glass) wato irin mai duhun nan haka ya dinga sharara gudu yana yi yana lallashi na sbd kukan da nakeyi. 

•••Alqawarin da Ciwo 10•••


Mun bar garin bauchi sosai sannan na saurara da kuka sbd na fara jin bacci, ido na a lumshe yaya aliyu ya dubeni yace" rahama ya akayi ne" na dago dara daran idanuna da suka zama tamkar an gulof sbd kuka na kalle shi nace " na am" yace kina jin baccine ? nace ' eh' ya ce "ok bari inyi parking sai kikoma baya ki kwanta ko? yayi parking a gafen hanya ya riko min hannu na fito na koma gidan baya na kwanta ya cire malim malim din da ke jikinsa ta lallausan shadda ya lilliba mini sannan ya koma mazauninsa ya ce gaba da tuku. ya zuge dukkan gilashan motar ya kunna mana A.C sannan ya saka mana kaset na turanci wakar celen dion ta (A NEW DAY HAS COME) tun ina jin wakar har sarkin barayi ya sace ni kwance ckn babbar rigar yaya aliyu ina shaker kamshin ni'imtaccen turarensa (HEAVEN).resemble amma gsky she is beautiful ko zaka ban aurenta idan tayi girma don na san yanzu karatu take ko?Yace ja bari sai ta girma in tana sonka sai in baka ita(second wife)suka yi dariya na kalli Aliyu alamar tambaya a ido na ya kashemin ido daya tare da roko hannuna yace to ismail sai gani na biyu,Yace yanzu kiri-kiri kunki tsayawa kuci abinci ko?Ko dan asmau bata nan 'matarsace asmau'Aliu yace wlh bahaka bane akwai abinci da muka taho dashi kasan kuma we are on our way kar muyi dare bisa hanya ga yarinyan mutane.Mukayi sallama dashi muka nufi mota sai da muka ci sinasir da miya wanda aka ciko mana kula dashi sannan muka kama hanya muna tafe muna hira abinmu.


✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨



Na shirya tsaf sannan na tsaya ina kollon yanayin dakin,gsky ya hadu kafet ya mamaye dakin ja sai labule a zagaye suma jajaye sai gado makeke da dressing mirro dinsa ga wardrob a manne a bango kai duk dai wani abu da zai kayata dakin an saka shi.Na fiti fslo na iske yana salla ganin haka sai na nemi kujera na nitse ins kallon tsarin falon shims ya hadu iya haduwa,babu abinda babu har wani guri naga an kebe a falon sbd yin karatu cike yar kantan take da littafan addini dana boko dirowar katakon dake falon kuwa shake take da electronics kayan wuta na zamani. Yana idar da sallah ya nufo guri na yace harkin kammala?Nima ina shigowa naga kina sallah shine na shiga wanka gashi har nayi sallah.Na gyada masa kai, bari in sa kayan bacci in zo muci abinci sai ki kwanta ko?" na gyada masa kai, kafin ya wuce dakinsa sai da ya kunna min tauraron dan adam sannan na ga ya haye benen da ka gidan ina tsammanin nan ne dakinsa. ya fito sanye ckn riga da wando ba bacci muka isa gun cin abinci, kula biyu ce daya sakwarace da miyar agushi wai shine nawa abincin dayan kuma salad ne shine nasa a yadda yace min shi baya cin abinci mai nauyi da dare. ya kawo mana juice da swan water muka ci muka sha. muna kammalawa ya riko hannuna muka shiga dakin da nayi sallah ya dubeni yace " kina jin bacci ko? na ce "' eh" ya ce , " to ga gado nan sai ki hau ki kwanta ni a dakin sama na ke kwana zaki iya kwana anan ko? ckn tsoro nace " ni ba zan iya ba ka san a gida ba na kwana ni kadai. gsky a gurinka zan kwana" yayi shiru yana tunani wai ashe shi yana son ya din ga nisanta ni da shine sbd kar ya kasance muna yawan cudanya da juna ya zamto ya karya alkawarin da ya daukar wa kansa. ya dubeni yace " kiyi hakuri ki kwanta a nan kinga can saman akwai sanyi da yawa" na make kafadata nace" ni dai na ki sai dai kazo nan mu kwana" yayi dan shiru sannan yace " shikenan zo muje dakin nawa" muna fitowa falo waya ta dinga ringing ya dauka suka gaisa da wanda ya bugo masa ina jin yana ce masa " eh wlh ban dade da dawowa ba, eh don Allah kar ka zo da safen ma hadu a ofis amma na san zan zo very late sbd wasu yan matsaloli. ok good nyt a gaida amaryar da ba ta tsufa" suka yi dariya tare da ajiye wayar. ya kalle ni tare da yin murmushi na lumshe ido na ya sake yin murmushi yace " duk baccin ne" come on let's go" gsky da muka shiga dakin baccin yaya aliyu rudewa nayi sai warware idanu nake ina kallo yadda ya kayata dakin(ALJANNAR DUNIYA) haka na fada a zuciya ta. wlh ni ban ma san yadda zan fadi irin shiryuwar dakin ba, yadda kasan a kasar waje haka yake. da yake gadon yaya aliyu makeke ne ko da muka kwanta akwai tazara tsakanin inda ya kwantar da ni da inda ya kwanta. domin kuwa mutum biyar zasu iya kwanciya a tsakiyarmu ba yare da wani ya matsi wani ba. in banda snyin kamshi babu abin da ke tashi a dakin, hatta bargin da ya lillibeni shima na sa kamshin daban, balle kuma shimfidar gadon yadda ka san anyi barin turare haka kamshi ke tashi. na saba a gida in zanyi bacci in rabu da jikin mutum amma yau sai ga aliyun da nake mannewa in yi bacci lokacin muna gida ya juyan baya. ban san lokacin da na mirgino na kankame shi ta baya ba. ina yan munfarfashi yace" menene kuma? na dauka kinyi bacci? nace " ni tsoro nake ji? yace " tsoron me?" nace " tsoron dodo" ya kyakyale da dariya yace" har yanzu rahama kina nan da wannan tsoron?to ki kwantar da hankalinki kiyi bcci ni daki na ba dodo" na dan fara masa yar shagwaba ta yace " ok don't cry bari in kunna fitila ki nuna min dodon"
follow me on facebook follow me on twitter follow me on instagram

Fitattun labarai

Habiba complete hausa novel

Amfanin cin qafar kaza

Budurwar Roba

Amfanin lemon tsami

Afanin Zogale

Adam A. Zango

Amfanin namijin Goro (bitter kola)

Tona asiri

Yanda zaka duba sunanka a Npower